Baibul a cikin shekara guda Maris 6
Markus 9:30-49 |
30. Suka bar wurin suka bi ta Galili. Yesu bai so wani yǎ san inda suke ba, |
31. domin yana koya wa almajiransa. Ya ce musu, “Za a ci amanar Ɗan Mutum, a ba da shi ga hannun mutane. Za su kashe shi, bayan kwana uku kuma zai tashi.” |
32. Amma ba su fahimci abin da yake nufi ba, suka kuma ji tsoro su tambaye shi game da wannan. |
33. Suka iso Kafarnahum. Da yana cikin gida, sai ya tambaye su, ya ce, “Gardamar me kuke yi a hanya?” |
34. Amma suka yi shiru, don a hanya suna gardama ne, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma? |
35. Da Yesu ya zauna, sai ya kira Sha Biyun, ya ce, “In wani yana so yǎ zama na fari, dole yǎ zama na ƙarshe duka, da kuma bawan kowa.” |
36. Ya ɗauki wani ƙaramin yaro ya sa yǎ tsaya a tsakiyarsu. Ya ɗauke shi a hannunsa, ya ce musu: |
37. “Duk wanda ya karɓi ɗaya daga cikin waɗannan ƙananan yara a cikin sunana, ni ya karɓa. Duk wanda kuma ya karɓe ni, ba ni ya karɓa ba, amma wanda ya aiko ni ne ya karɓa.” |
38. Yohanna ya ce, “Malam mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, sai muka ce yǎ daina, domin shi ba ɗaya daga cikinmu ba ne.” |
39. Yesu ya ce, “Kada ku hana shi. Ba wanda yake yin ayyukan banmamaki a cikin sunana, nan take yǎ faɗi wani abu mummuna game da ni. |
40. Gama duk wanda ba ya gāba da mu, namu ne. |
41. Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ba ku ruwan sha a sunana, saboda ku na Kiristi ne, lalle, ba zai rasa ladarsa ba. |
42. “Da dai wani yǎ sa ɗaya daga cikin waɗannan ʼyan yara masu gaskatawa da ni yǎ yi laifi, zai fiye masa a rataya wani babban dutsen niƙa a wuyarsa, a jefa shi cikin teku. |
43. In hannunka yana sa ka yin zunubi, yanke shi. Ai, gwamma ka shiga rai da hannu ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta, inda ba a iya kashe wutar ba, da hannuwanka biyu. |
44. *** |
45. In kuma ƙafarka tana sa ka yin zunubi, yanke ta. Ai, gwamma ka shiga rai da ƙafa ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da ƙafafunka biyu. |
46. *** |
47. In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi. Ai, gwamma ka shiga mulkin Allah da ido ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da idanu biyu, |
48. inda “ ‘tsutsotsinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a iya kashewa.’ |
49. Za a tsarkake kowa da wuta. |
|