Baibul a cikin shekara guda Fabrairu 22
Markus 3:20-35 |
20. Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba. |
21. Da ʼyanʼuwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.” |
22. Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Beʼelzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.” |
23. Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai, ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan? |
24. In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba. |
25. In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba. |
26. In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan. |
27. Hakika, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yǎ kwashe dukiyarsa, sai bayan ya ɗaure mai ƙarfin, saʼan nan zai iya yin fashin gidansa. |
28. Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi. |
29. Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” |
30. Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.” |
31. Sai mahaifiyar Yesu tare da ʼyanʼuwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yǎ kira shi. |
32. Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da ʼyanʼuwanka suna waje, suna nemanka.” |
33. Ya yi tambaya, ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da ʼyanʼuwana?” |
34. Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi, ya ce, “Ga mahaifiyata da ʼyanʼuwana! |
35. Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗanʼuwana, da ʼyarʼuwata, da kuma mahaifiyata.” |
|